Ambaliya Ta Halaka Fiye da Mutane 100 a Jihar Neja
Kwanan wata: 30 Mayu, 2025 | Marubuci: Wakilinmu na Neja
Wakilin Pan Africa News Agency ya gano cewa unguwanni da dama da suka hada da Tiffin Maza, Anguwan Hausawa da Kpakungu sun fi fuskantar barnar ruwa, lamarin da ya tilasta wa jama’a tserewa zuwa tsaunuka da makarantun gwamnati da aka mayar da su sansanin wucin gadi.
Martanin Gwamnati
Gwamnatin Jihar Neja ta bayyana halin da ake ciki a matsayin bala’in kasa, inda Gwamna Umaru Bago ya bayar da umarnin kafa kwamiti na gaggawa domin bai wa wadanda lamarin ya shafa agajin farko.
“Zamu hada kai da NEMA da sauran hukumomi don tabbatar da cewa rayukan jama’a sun samu kariya,” in ji Gwamna a cikin wata sanarwa da ofishinsa ya fitar.
Kalubalen Tsaro da Muhalli
Masana harkar muhalli na ganin cewa irin wadannan ambaliya na kara yawaita sakamakon dumamar yanayi da kuma rashin gyara dam-dam da madatsun ruwa da ke cikin kasar.
“Wannan bala’i ya sake tunatar da mu cewa lokaci ya yi da Najeriya da sauran kasashen Afrika za su dauki matakan kare muhalli da gina ingantattun hanyoyin ruwa,” in ji Malam Nura Usman, masanin muhalli daga Jami’ar Abuja.
Rayuwa Bayan Ambaliya
Wadanda suka tsira daga ambaliyar sun bayyana halin kuncin da suke ciki. “Mun rasa komai—gidaje, kayan amfanin gona, dabbobi. Muna bukatar taimako cikin gaggawa,” in ji Aisha Yusuf, wata uwa mai yara hudu da ke kwance a sansanin wucin gadi.
Kungiyoyin agaji na cikin gida da na kasa da kasa sun fara tura kayayyakin taimako, ciki har da abinci, bargo da magunguna zuwa yankin Mokwa da ke cikin Jihar Neja.